Masu garkuwa da mutane sun sace tsohon general manager na hukumar tashar jiragen ruwa a kano

Anyi garkuwa da tsohon general manager na hukumar kula da tashohshin jiragen ruwa ta kasa Bashir M Abdullahi a Kano.

Anyi garkuwa da shi ne a yammacin yau laraba a gonarsa da ke kauyen Gomo a karamar hukunar Sumaila.

Wani mazaunin kauyen na Gomo ya ce wasu Yan bindiga da ba'a san ko suwa ye ba ne su kai awon gaba da shi a yayin da yake duba gonarsa da ke kauyen.

Yayin da aka tuntubi kakakin rundunar 'yan sandan jihar Kano DSP Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa ba shi da masaniya a kan lamarin, amma zai bincika ya sanar da hakikanin lamarin.

Comments

Popular posts from this blog

Dana ba zai ci amanarki ba saboda kina da kyau – Tsohon gwamna ga surukarsa

SOJOJI SUN HALAKA KASURGUMIN DAN AWAREN KASAR BIAFRA.